IQNA

Mutane 60 Bayan Ruftawar Guinin Coci A Najeriya

22:16 - December 11, 2016
Lambar Labari: 3481026
Bangaren kasa da kasa, Mutane kimanin 60 ne suka mutu bayan da ginin wani coci ya rufta a birnin Uyo na jahar Akwa Ibom a kudancin Najeriya.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shagfin alalam cewa, rahotanni sun ce Majami'ar Reigners Bible Church, ta cika makil saboda ana bikin nada shugabanta a matsayin Bishop a lokacin da lamarin ya faru.

Wasu daga cikin kafafen yada labarai a Najeriya sun ambato wadanda suka shaida lamarin na cewa ana kan yi wa ginin kwaskwarima saboda hasashen cewa jama'a da dama za su halacci taron.

An sa ran Gwamnan jihar Udom Emmanuel zai halarci taron, amma rahotanni sun ce ba ya wurin lokacin da hadarin ya faru.

Rahotannin sun tabbatar da cewa an garzaya da wadanda suka ji raunuka zuwa asibitoci da dama a fadin birnin.

Ana yawan samun ruftawar gine-gine a Najeriya, abin da masu sharhi ke alakanta wa da rashin bin doka da amfani da kayan aiki marasa kyau.

Mutane da dama ne suka mutu a watan Satumbar 2014 lokacin da wani ginin ya rufta a unguwar Lagon da ke cikin birnin Lagos.

3552750


captcha