Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na hukumar kula da al’adun muslunci cewa, a yayin azumin watan Ramadan, mai baiwa Iran shawara kan al’adu a kasar Tanzaniya ya gudanar da gasar kur’ani mai tsarki ta yanar gizo.
A wannan gasa, an bukaci masu sauraro da su saka karatun nasu a matsayin gajeren bidiyo a shafinsu da kuma a rubutun da ya dace a shafin wakilan ma’aikatar al’adu ta Iran.
A cikin wannan gasa, an ba wa mahalarta 4 da suka lashe mafi kyawun bidiyoyin kallo an ba su kyautuka na zane.
Yasin Mohammad Haruna, Zulnaila Mohammad Ali, Mustafa Mekunga da Mohammad Abdullah Makdam an zabi (na daya zuwa hudu) bi da bi.