IQNA

Hasumiyar Wani Tsohon Masallaci Da Ta Yi Saura A Kan Ruwa Bayan Nutsewar Masallacin A Turkiya

19:56 - February 23, 2021
Lambar Labari: 3485684
Tehran (IQNA) Hasumiyar wani tsohon masallaci da ya nutse a cikin ruwa ta yi saura a kan ruwa  a kasar Turkiya

Jaridar Daily Sabah ta bayar da rahoton cewa, a cikin lardin Aghari na kasar Turkiya, wata hasumiyar wani tsohon masallaci da ya nutse a cikin ruwa ta yi saura a kan ruwa, inda har yanzu take tsaye ba tare da ta fadi ba.

Wannan lamarin ya faru ne a kauyen Bash Jawish da ke cikin lardin Aghari, bayan gina wata babbar madatsar ruwa, wanda hakan ya yi sanadiyyar nutsewar gine-ginen kauyen da dama, da hakan ya hada har da wani tsohon masallaci da ke yankin.

Babbar koramar da ke yankin ce ta cinye gidaje da sauran gine-gine da suka hada hard a na masallacin, amma abin mamaki shi ne yadda har yanzu hasumiyar masallacin take tsaye.

Wannan yanki dai yana  agabashin kasar Turkiya ne, kuam yanki ne da ake fama da sanyi a lokacin hunturu, inda dusar kankara kan rufe yankin baki daya, wannan korama kuma tana daskarewa ta koma kankara har zuwa karshen lokacin hunturu.

3955338

 

 

 

captcha