Kamfanin dillancin labaran iqna, a wata wasika da babban kwamandan na kungiyar Hizbullah ya aikewa da ministan harkokin wajen na jamhuriyar musulunci ta Iran, Sayyid Hassan Nasarallah ya ce;
Na rubuto muku wasika ne saboda in bayyana goyo baya da girmamawa a gare ku,saboda shigar da ku cikin jerin sunayen daukaka.
Sayyid Nasarallah yana ishara ne da jerin sunayen mutanen da Amurka take kakabawa takunkumi da a bayan nan ta shigar da sunan ministan harkokin wajen na Iran.
A cikin wasikar, babban sakataren kungiyar ta Hizabullah ya bijiro da yadda yakin kwanaki 33 na 2016 ya kasance ta fuskar diplomaisyya, da yadda sakataren harkokin wajen Amurka ya bukaci a tsagaita wutar yaki.