Kamfanin dillancin labaran iqna, ya bayar da rahoton cewa, ofishin bababn hafsan hafsoshin rundunar sojin kasar ta Myanmar ne ya sanar da hakan a jiya Juma'a, a wani mataki na neman ganin an shiga tattaunawa da musulmin.
bayanin ya ce wannan matakin daga bangaren sojoji ne, kuma za su bayar da dama daga nan har zuwa 30 ga watan Afirilun 2019 ga musulmi 'yan aware da su sanya hannu kan yarjejeniyar dakatar da bude wuta.
Wannan dai shi ne karon farko da rundunar sojin kasar Myanmar ta taba sanar da dakatar da bude wuta daga bangarenta kan musulmin Rohingya a cikin shekaru fiye da talatin da take kaddamar da farmakin sojia kansu lokaci zuwa lokaci.
Myanmar dai na fuskantar babban matsain lamba daga kasashen duniya, dangane da kisan kiyashin da sojojin kasar da kuma 'yan addini buda masu tsatsauran ra'ayi suka yi kan musulmi daga shekara ta 2015 ya zuwa yanzu.