IQNA

Gasar Kur’ani Ta Daliban Azhar A Cikin Watan Maris

20:18 - January 16, 2018
Lambar Labari: 3482304
Bangaren kasa da kasa, a cikin watan maris mai zuwa ne za a gudanar da bangaren karshe na gasar Kur’ani mai tsarki ta jami’ar Azhar.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakaltodaga shafin sadal balad cewa, Salen Abbas shugaban bangaren kula da harkokin gasar kurni na jami’ar Azaar ya ce, a cikin watan maris mai zuwa ne za a gudanar da bangaren karshe na kasar Kur’ani mai tsarki ta jami’ar, inda bangarorin harda za su kasance a bangaren hardar kur’ani baki daya, juzui 25, juzui 18.

Ya ci gaba da cewa ya zuwa yanzu an kammala dukkanin shirye-shiryen da suka kamata domin gudanar da wannan gasa ta hardar kur’ani mai tsarki ta jami’ar azahar da ake yi duk shkara.

Tun a cikin watan da ya gabata ne dai aka fara gasar a matsayin share fage, musamman ganin cewa masu shiga gasar adadinsu yana da yawan gaske.

A yayin gudanar da gasar a matakin karshe babban malmin Azhar da wasu daga cikin malaman jami’an jami’ar gami da wasu jami’an gwamnatin Masar duk za su halartar, kuma za a bayar da kyautuka na musaman ga wadanda suka fi nuna kwazo.

Abin tuni a nan da shi ne, cibiya Azaha ita ce babbar cibiyar ilmimi ta mabiya mazhabobin ahlu sunna a duniya baki daya, wadda aka gina ta tun kimanin shekaru dubu daya da suka gabata.

3682522

 

captcha